GidaAzkarDaga cikin falalar tasbihi da tahmidizikiri 9

Daga cikin falalar tasbihi da tahmidi — zikiri 9

فضل التسبيح و التحميد، و التهليل، و التكبير · Hisnul Muslim · 9 / 12

Karanta · SauraraFayilar PDF

جَاءَ أَعْرَابِيٌّ إِلَى رَسُولِ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم فَقَالَ: عَلِّمْنِي كَلاماً أَقُولُهُ: قَالَ: ((قُلْ: لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، اللَّهُ أَكْبَرُ كَبِيراً، وَالْحَمْدُ لِلَّهِ كَثِيراً، سُبْحَانَ اللَّهِ رَبِّ العَالَمِينَ، لاَ حَوْلَ وَلاَ قُوَّةَ إِلاَّ بِاللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَكِيمِ)) قَالَ: فَهَؤُلاَءِ لِرَبِّي، فَمَا لِي؟ قَالَ: ((قُلْ: اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي، وَارْحَمْنِي، وَاهْدِنِي، وَارْزُقْنِي)).

Ma’ana: Wani balaraben karkara ya zo wajen Manzon Allah, tsira da a mincin Allah su tabbata a gareshi, sai ya ce: Koya mini wadansu kalmomi da zan rika fada. Sai ya ce: “Ka ce: Babu abin bautawa da cancanta sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, Allah ne mafi girma, ina girmama shi girmamawa, kuma godiya ta tabbata ga Allah da yawa, tsarki ya tabbata ga Allah, Ubangijin halittu. Babu dabara kuma babu karfi sai ga Allah mabuwayi mai hikima. Sai mutumin ya ce: Wadannan na Ubangijina ne, ni kuma nawa fa? Sai ya ce: Ka ce: Ya Allah Ka yi mini gafara, ka ji kai na ka shiryar da ni, ka azurtani.

Saurara · Muryar Hamad al-Duraiham

Azkar · 15 harsuna