كَانَ الرَّجُلُ إِذَا أَسْلَمَ عَلَّمَهُ النَّبيُّ صلى الله عليه وسلم الصَّلاَةَ ثُمَّ أَمَرَهُ أَنْ يَدْعُوَ بِهَؤُلاَءِ الْكَلِمَاتِ: ((اللَّهُمَّ اغْفِرِ لِي، وَارْحَمْنِي، وَاهْدِنِي، وَعَافِنِي وَارْزُقْنِي)).
Ma’ana: ldan mutum ya musulunta sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya koya masa sallah, sannan ya umurce shi ya rika addu‘a da wadannan kalmomi: “Ya Allah ka gafarta mini, ka ji kai na, ka shiryar da ni, ka amintar da ni daga bala’i ka azurtani.
Saurara · Muryar Hamad al-Duraiham