GidaAzkarZikirin tashi daga baccizikiri 4

Zikirin tashi daga bacci — zikiri 4

أذكار الاستيقاظ من النوم · Hisnul Muslim · 4 / 4

Karanta · SauraraFayilar PDF

﴿ إِنَّ فِي خَلْقِ السَّمَوَاتِ وَالأَرْضِ وَاخْتِلاَفِ اللَّيْلِ وَالنَّهَارِ لَآيَاتٍ لأُوْلِي الألْبَابِ * الَّذِينَ يَذْكُرُونَ اللَّهَ قِيَاماً وَقُعُوداً وَعَلَىَ جُنُوبِهِمْ وَيَتَفَكَّرُونَ فِي خَلْقِ السَّمَوَاتِ وَالأَرْضِ رَبَّنَا مَا خَلَقْتَ هَذا بَاطِلاً سُبْحَانَكَ فَقِنَا عَذَابَ النَّارِ* رَبَّنَا إِنَّكَ مَن تُدْخِلِ النَّارَ فَقَدْ أَخْزَيْتَهُ وَمَا لِلظَّالِمِينَ مِنْ أَنصَارٍ* رَّبَّنَا إِنَّنَا سَمِعْنَا مُنَادِياً يُنَادِي لِلإِيمَانِ أَنْ آمِنُواْ بِرَبِّكُمْ فَآمَنَّا رَبَّنَا فَاغْفِرْ لَنَا ذُنُوبَنَا وَكَفِّرْ عَنَّا سَيِّئَاتِنَا وَتَوَفَّنَا مَعَ الأبْرَارِ* رَبَّنَا وَآتِنَا مَا وَعَدتَّنَا عَلَى رُسُلِكَ وَلاَ تُخْزِنَا يَوْمَ الْقِيَامَةِ إِنَّكَ لاَ تُخْلِفُ الْمِيعَادَ* فَاسْتَجَابَ لَهُمْ رَبُّهُمْ أَنِّي لاَ أُضِيعُ عَمَلَ عَامِلٍ مِّنكُم مِّن ذَكَرٍ أَوْ أُنثَى بَعْضُكُم مِّن بَعْضٍ فَالَّذِينَ هَاجَرُواْ وَأُخْرِجُواْ مِن دِيَارِهِمْ وَأُوذُواْ فِي سَبِيلِي وَقَاتَلُواْ وَقُتِلُواْ لأُكَفِّرَنَّ عَنْهُمْ سَيِّئَاتِهِمْ وَلأُدْخِلَنَّهُمْ جَنَّاتٍ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الأَنْهَارُ ثَوَاباً مِّن عِندِ اللَّهِ وَاللَّهُ عِندَهُ حُسْنُ الثَّوَابِ * لاَ يَغُرَّنَّكَ تَقَلُّبُ الَّذِينَ كَفَرُواْ فِي الْبِلاَدِ * مَتَاعٌ قَلِيلٌ ثُمَّ مَأْوَاهُمْ جَهَنَّمُ وَبِئْسَ الْمِهَادُ * لَكِنِ الَّذِينَ اتَّقَوْاْ رَبَّهُمْ لَهُمْ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِنْ تَحْتِهَا الأَنْهَارُ خَالِدِينَ فِيهَا نُزُلاً مِّنْ عِندِ اللَّهِ وَمَا عِندَ اللَّهِ خَيْرٌ لِّلأَبْرَارِ * وَإِنَّ مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ لَمَن يُؤْمِنُ بِاللَّهِ وَمَا أُنزِلَ إِلَيْكُمْ وَمَآ أُنزِلَ إِلَيْهِمْ خَاشِعِينَ لِلَّهِ لاَ يَشْتَرُونَ بِآيَاتِ اللَّهِ ثَمَناً قَلِيلاً أُوْلَئِكَ لَهُمْ أَجْرُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ إِنَّ اللَّهَ سَرِيعُ الْحِسَابِ*يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُواْ اصْبِرُواْ وَصَابِرُواْ وَرَابِطُواْ وَاتَّقُواْ اللَّهَ لَعَلَّكُمْ تُفْلِحُونَ ﴾

Ayoyin guma 11 na karshe suratul Al imrana. (wato fadin Allah mai girma da daukaka): Ma’ana: Lalle a cikin halittar sammai da kasa, da kuma jujjuyawar dare da yini to akwai abubuwan la’akari ga ma’aboda hankula. Su ne wadanda suke anbaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma gefan jukkunansu, kuma suna tunani a halittar sammai da kasa, (suna cewa Ya) Ubangijin mu ba ka halicci wannan don wasa ba, tsarki ya tabbata a gareka to ka tsare mu azabar wuta. (Ya) Ubangijn mu! Lalle ne kai duk wanda ka shigar da shi wuta to hakika ka tozartar da shi, kuma kafirai ba su da mataimaka. (Ya) Ubangijin mu! Lalle ne mu mun ji maishela yana kira akan ku yi imani da Ubangijinku to mun yi imani, (Ya) Ubangijin mu ka gafarta mana zunuban mu, kuma ka kankare mana laifukan mu kuma ka dauki rayukan mu tare da mutanan kwarai. (Ya) Ubangijin mu! Kuma ka ba mu abinda ka yi mana alkawarinsa akan (har sunan) Manzanninka, kuma kada ka kunyata mu ranar alkiyama, lalle ne kai ba ka saba alkawari. Sai Ubangijin su ya amsa musu (cewa) lalle ni ba na tozartar da aikin mai aiki daga cikinku daga namiji ko mace, sashinku daga sashi, to dukkan wadanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidajansu aka kuma cutar da su akan hanya ta, kuma suka yi yaki kuma aka kashe su hakika zan kankare musu laifukansu kuma hakika zan shigar da su gidaje na aljanna da koramu suke gudana daga karkashinsu (wannan) ladane daga wurin Allah, kuma Allah a wurinsa ne kyakkyawan lada yake. Kada jujjuyawar da kafirai suke yi a garuruwa ya rudar da kai. Jin dadine kadan, sannan makomarsu jahannama, kuma ta yi muni ta zama shinfida. Saidai dukkanin wadanda suka ji tsoron Ubangijinsu suna da gidaje na aljanna da koramu suke gudana daga karkashin su masu dawwamane a cikinta, garace daga wurin Allah, kuma abinda yake a wurin Allah shi ne ya fi ga mutanan kwarai. Kuma hakika akwai daga cikin wadanda aka baiwa littafi wadanda tabbas suna yin imani da Allah da kuma abinda aka saukar zuwa gareku da kuma abinda aka saukar zuwa garesu suna masu kankan-da-kai ga Allah, ba sa musanya ayoyin Allah da kudi kadan, wadannan suna da ladansu a wurin Ubangijinsu, lalle Allah mai saurin hisabi ne. Ya ku wadanda suka yi imani! Ku yi hakuri ku cije kuma ku yi dako ku ji tsoron Allah domin ku rabauta. (Suratu Ali Imran, aya ta:190-200).

Saurara · Muryar Hamad al-Duraiham

Azkar · 15 harsuna